Gwamnatin Najeriya ta gurfanar da shugaban kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah kan ta’addanci.

top-news


Gwamnatin tarayyar Najeriya ta shigar da karar shugaban kungiyar Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Bodejo da ake tsare da shi a matsayin shugaban kungiyar ta'addanci.

A tuhumar ta’addanci da aka yi ranar 12 ga watan Maris, an zargi Bodejo da zagon kasa ga tsaron Najeriya ta hanyar kafa kungiyar ‘yan bindiga da kuma ba da makamai ba tare da izini ba.

Wani bangare na tuhume-tuhumen ya kara da cewa: “Kai Bello Bodejo, Namiji, Babba, a ranar 17 ga Janairu, 2024, ko kafin ranar 17 ga watan Janairu, 2024, a Lafia, Jihar Nasarawa, da ke karkashin ikon wannan Kotu mai girma, ka aikata laifin da za a ce: kun kafa wata kungiya da aka fi sani da Kungiyar Zaman Lafiya ba tare da izini ba, kuma ta haka ne kuka aikata wani abu da ya saba wa tsaron kasa da kare lafiyar al’umma, laifin da ake hukunta shi a karkashin sashe na 29 na dokar ta’addanci (Rigakafin da Hana) ta 2022.”

An kama Bodejo ne a ranar 23 ga watan Janairu a ofishin Miyetti Allah da ke karamar hukumar Karu a jihar Nasarawa bisa zargin fallasa tare da ba wa kungiyar ‘yan banga makamai.

Babban Lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi (SAN), ya shigar da kara a ranar 5 ga watan Fabrairu yana neman a ci gaba da tsare Bodejo har sai lokacin da DIA ta kammala binciken da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

Mai shari’a Inyang Edem Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja, bisa karar da aka shigar, ya bayar da umarnin a tsare Bodejo na tsawon kwanaki 15.

A lokacin da wa’adin kwanaki 15 ya kare a ranar 22 ga watan Fabrairu, alkalin kotun ya baiwa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki bakwai ta shigar da karar Bodejo.

Sai dai a zaman da aka yi a ranar Laraba, Hukumar Leken Asiri ta Defence (DIA) da ke Abuja ta ki gabatar da Shugaban Miyetti Allah a gaban Babbar Kotun Tarayya domin gurfanar da shi a gaban kuliya.

Bayan rashin halartar wanda ake tsare da shi a kotu, Mai shari’a Ekwo ya tambayi lauyan gwamnatin tarayya, Y.A. Imana, akan rashin gurfanar da Bodejo a gaban kotu.

Lauyan gwamnati, ya bayyana cewa an shigar da karar ne a jiya, sai dai alkalin ya yi mamakin dalilin da ya sa ba a gabatar da wanda ake zargin gabansa ba.

A wannan lokaci, lauyan Bodejo, Mohammed Sheriff, ya shaida wa Kotun cewa ya shigar da kara ne na neman a sake shi ba tare da wani sharadi ba daga hannun hukumar leken asiri ta tsaro.

Lauyan ya roki kotun da ta saurari bukatar belin wanda yake karewa.

Ya ce, "Takardar neman belinmu ta kasance ranar 26 ga Fabrairu, 2024, kuma muna neman a shigar da mai neman belin kafin a gurfanar da shi a gaban kotun da ta dace."

Sai dai lauyan masu shigar da kara, Y.A Imana, ya nuna kakkausar suka ga bukatar belin wanda ake tsare da shi, saboda tuhumar da ake masa na da alaka da zagon kasa ga tsaron tarayyar Najeriya, inda ya bukaci kotun da ta yi watsi da bukatar.

Mai shari’a Ekwo, bayan da ya amshi hujjoji daga lauyoyin, ya sanya ranar 22 ga watan Maris domin yanke hukunci kan ko a amince da bukatar belin ko a’a.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *